Most searched:

Shaidar Zul-Shahadatain Kan Wilayar Jagoran Masu Taqawa

Khuzayma ɗan Sabit, wanda ake yi wa laƙabi da “Zul-Shahadatain”, yana daga cikin Sahabban Manzon Allah (Tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa) kuma daga cikin sahabban Amirul Muuminiin Ali (Amincin Allah ya tabbata a gare shi). Cikamakin Annabawa ya sanya masa laƙabin “Zul-Shahadatain” saboda an karɓi shaidarsa a matsayin shaidar mutum biyu. A ƙarshe, Khuzayma ya yi shahada a Yaƙin Siffin.

Khuzayma ɗan Sabit al-Ansari yana daga cikin fitattun Ansar, Sahabban Manzon Allah da kuma amintattun sahabban Jagoran Masu Taqawa. Ya fito daga ƙabilar Aws, kuma yana daga cikin mutanen Madina na farko da suka karɓi Musulunci. Ya kuma farfasa gumakan ƙabilarsa, Banu Khatma. (1)

A ƙarshe, a ranar tara ga watan Safar na shekara ta 37 bayan Hijira, yayi yaƙi cikin cikakkiyar jarumta a ƙarƙashin tutar Amirul Muuminiin (Amincin Allah ya tabbata a gare shi) a Yaƙin Siffin, har yayi shahada.

Rashin Yin Mubaya’a ga Abu Bakr

Bayan rasuwar Manzon Allah a shekara ta 11 bayan Hijira, an kafa majalisar Saqifa a Madina, kuma aka zaɓi Abu Bakr a matsayin halifa. Wannan zaɓi ya fuskanci adawa daga wasu Sahabbai waɗanda suka ƙi yin mubaya’a ga Abu Bakr.

Daya daga cikinsu shi ne Khuzayma ɗan Sabit, amintaccen Sahabin Cikamakin Annabawa kuma daga cikin sahabban Amirul Muuminiin (Amincin Allah ya tabbata a gare shi). Khuzayma ɗan Sabit ya ƙi yin mubaya’a ga Abu Bakr saboda imaninsa da haƙƙin Jagoran Masu Taqawa na halifanci. (2)

Shaida Kan Ghadir Khumm

Amirul Muuminiin (Amincin Allah ya tabbata a gare shi), a Rahabar Kufa, ya nemi mutane su bayar da shaida game da abin da ya faru a Ghadir Khumm. A wannan wuri, Khuzayma ɗan Sabit da wasu Sahabbai suka bayar da shaida kan wilayar Jagoran Masu Taqawa.

Amirul Muuminiin Ali (Amincin Allah ya tabbata a gare shi), a yankin Rahaba, ya rantsar da mutane ya ce:

“Duk wanda ya ji abin da Manzon Allah (Tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa) ya faɗa a ranar Ghadir Khumm, ya tashi. Kada kowa ya tashi sai wanda da da kansa yaji daga Manzon Allah.”

A wannan lokacin, sama da mutum goma suka tashi, kuma Khuzayma ɗan Sabit yana daga cikinsu. Suka ce:

“Muna shaida cewa mun ji Manzon Allah (Tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa) yana cewa: Ku sani cewa Allah Madaukakin Sarki ne Waliyyina kuma Mai kula da ni, ni kuma Waliyyi ne kuma Mai kula da muminai. Ku sani, duk wanda nake Mawlansa, to Ali ma Mawlansa ne. Ya Allah! Ka so wanda ya so shi, Ka ƙi wanda ya ƙi shi, Ka ƙaunaci wanda ya ƙaunace shi, Ka yi gaba da wanda ya yi gaba da shi, kuma Ka taimaki wanda ya taimake shi.” (3)

Mubaya’a ga Jagoran Masu Taqawa

An yi mubaya’a ga Amirul Muuminiin (Amincin Allah ya tabbata a gare shi) a matsayin halifa a Madina, tare da halartar fitattun mutane masu tasiri a cikin al’ummar Musulmi. Daga cikin waɗanda suka yi masa mubaya’a akwai Khuzayma ɗan Sabit, ɗaya daga cikin shahararrun Sahabban Manzon Allah. (4)

Waƙar Yabon Amirul Muuminiin (Amincin Allah ya tabbata a gare shi)

Khuzayma yana da baiwar waƙa, kuma ya rera waƙoƙi domin yabawa da goyon bayan Amirul Muuminiin (Amincin Allah ya tabbata a gare shi).

Lokacin da mutane suka yi mubaya’a ga Amirul Muuminiin Ali (Amincin Allah ya tabbata a gare shi), Khuzayma ɗan Sabit ya rera wannan waƙa:

“Lokacin da muka yi mubaya’a ga Ali (Amincin Allah ya tabbata a gare shi), Abu al-Hassan ya isar mana wajen tsoron fitina.

Mun same shi a matsayin wanda ya fi kowa cancanta da mulki.

Shi ne wanda ya fi kowa sanin Al-Qur’ani da Sunnar Annabi.

Quraishawa ba za su iya kaiwa ga ƙurar sawunsa ba, ko da wata rana suka hau rakuma sirara masu saurin gudu.

Duk wani alheri da yake cikinsu gaba ɗaya ya taru a cikin Ali (Amincin Allah ya tabbata a gare shi), kuma kyawun halayen da Imam yake da su babu su a wajen ko ɗaya daga cikinsu.

Wasiyyin Manzon Allah (Tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa) shi kaɗai ne daga cikin Aali nasa, kuma tun zamanin da shi ne jarumin mahayin Manzon Allah.

A cikin mutane, shi ne na farko da ya tsayar da sallah, sai dai mafi alherin mata, kuma Allah ne Mai baiwa.

Shi ne gwarzon al’umma a duk wani lamari mai tsanani da firgici, lokacin da rayukan jarumai suke kaiwa ga maƙogwaronsu.

Shi ne wanda ake nuna wa da yatsu, kuma shi ne Imam na kowa. Zan cigaba da wannan imani har sai an rufe ni cikin likkafani.” (5)

Halarta a Yaƙin Siffin

Khuzayma ɗan Sabit ya halarci Yaƙin Siffin tare da Amirul Muuminiin Ali (Amincin Allah ya tabbata a gare shi), amma a farko ya ƙi shiga yaƙin kai tsaye. Yana jira ne har hasashen Cikamakin Annabawa game da shahadar Ammar ɗan Yasir ya tabbata.

Khuzayma ɗan Sabit al-Ansari ya halarci Yaƙin Siffin ya ce:

“Ba zan tsaya a bayan kowane kwamanda ba, kuma ba zan yi yaƙi ba har sai an kashe Ammar, in ga wanda zai kashe shi, domin na ji Manzon Allah yana cewa: Ƙungiyar azzalumai ce za ta kashe Ammar.”

Lokacin da aka kashe Ammar, Khuzayma ya ce:

“Yanzu lokaci ya yi da zan cika alhakina.”

Sannan ya nufi fagen yaƙi, ya yi yaƙi har shi ma ya yi shahada. (6)

Yaƙi Har Zuwa Ƙarshen Rai

Shahadar Khuzayma ɗan Sabit a Yaƙin Siffin ta faru ne a lokacin da wutar yaƙin ta yi tsanani ƙwarai. Ta zama babbar asara ga rundunar Amirul Muuminiin Ali (Amincin Allah ya tabbata a gare shi), amma ta nuna cikakkiyar biyayyarsa da sadaukarwarsa a tafarkin Musulunci.

A Yaƙin Siffin, bayan shahadar Ammar da Ibn al-Tihan, Khuzayma ɗan Sabit ya fito yana yin wannan rajazi:

“Mutum mai jira, yaya tsawon burinsa na rayuwa yake, alhali an miƙa mutane ga wasu, kuma magada suna cikinsu?

Ga Ali nan, kuma duk wanda ya ƙi biyayya gare shi ya karya alƙawari .”

Sannan ya yi yaƙi har yayi shahada. (7)

Matsayin Khuzayma a Wajen Jagoransa

Bayan abin da ya faru a Siffin, Amirul Muuminiin (Amincin Allah ya tabbata a gare shi), a wani ɓangare na ɗaya daga cikin hudubobinsa a Kufa, ya ambaci sunayen wasu daga cikin sahabbansa na musamman cikin baƙin ciki da nadama. Zul-Shahadatain yana daga cikinsu.

Amirul Muuminiin (Amincin Allah ya tabbata a gare shi) ya ce:

“Eh, waɗannan ’yan’uwan da aka zubar da jininsu a Yaƙin Siffin ba su yi asara ba, duk da cewa ba sa nan yau domin abincinsu ya zama baƙin ciki da damuwa, abin shansu kuma ya zama jinin zuciya. Wallahi, sun haɗu da Allah, Ya ba su ladansu, kuma bayan lokacin tsoro da wahala, Ya saukar da su a gidan amincinsa.

Ina ’yan’uwana waɗanda suka bi tafarkin gaskiya kuma suka rasu a kan gaskiya? Ina Ammar? Ina ɗan Tihan? Ina Zul-Shahadatain, Khuzayma ɗan Sabit? Ina kuma makamantansu daga cikin ’yan’uwansu, waɗanda suka ɗaura alƙawarin sadaukar da rai, kuma aka aika da kawunansu zuwa ga azzalumai?”

Sannan ya kama gemunsa mai albarka, ya yi kuka na tsawon lokaci, ya ce:

“Ah, na yi kewar ’yan’uwana waɗanda suka karanta Al-Qur’ani, suka yi hukunci da shi, suka yi tunani a kan farillan Allah suka tsayar da su, suka raya Sunnonin Allah suka kawar da bidi’o’i, suka amsa kiran Jihadi, suka amince da jagoransu kuma suka bi shi.”

Sannan ya ɗaga murya ya ce:

“Jihadi! Jihadi! Ya ku bayin Allah! A yau zan shirya runduna. Duk wanda yake shauƙin haɗuwa da Allah, ya fita tare da mu.” (8)

Majiyoyi

  1. Ibn Athir, Usud al-Ghaba fi Ma’rifat al-Sahaba; Ibn Hajar al-Asqalani, Al-Isaba fi Tamyiz al-Sahaba.
  2. Al-Sahih min Sirat al-Nabi al-A’azam, juzu’i na 33, shafi na 304.
  3. Awalim al-Ulum, juzu’i na 15, shafi na 236.
  4. Al-Tabaqat al-Kubra, juzu’i na 3, shafi na 22.
  5. Bihar al-Anwar, juzu’i na 32, shafi na 34.
  6. Kashf al-Ghumma fi Ma’rifat al-A’imma, juzu’i na 1, shafi na 260.
  7. Bihar al-Anwar, juzu’i na 32, shafi na 587.
  8. Nahjul Balagha, Huduba ta 182.

Ƙarin abubuwa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *