Haihuwar Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa)
A bisa ra’ayin malaman Shi’a, an haifi Shugaban Annabawa Muhammad al-Musɗafa (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa) a lokacin fitowar alfijir na ranar 17 ga watan Rabi’ul Awwal, wanda ya kasance ranar Juma’a, a Makka mai tsarki. Haihuwarsa mai albarka ta yi daidai da lokacin mulkin Anushirwan mai adalci, kuma a wannan shekarar ne aka halaka rundunar giwaye.
Sunansa shi ne Muhammad (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa), kunyarsa kuwa Abul Qasim ce. Sunan mahaifinsa Abdullah ne, sunan mahaifiyarsa kuma Amina ‘yar Wahab ce.
A lokacin haihuwarsa, haske ya bayyana daga goshinsa mai daraja, kuma kamshin miski ya fitowa daga gare shi. Wani haske ya haskaka daga yankin Hijaz a wannan dare, sannan ya bazu a duk duniya. Kujerun sarakuna sun fadi, kuma dukkan su sun kasance kurame a wannan rana ba sa iya magana. Mala’iku makusanta da kuma tsarkakkun ruhin annabawa sun halarci lokacin haihuwarsa. Ridwan, mai kula da Aljanna, ya sauko tare da hurul’in, suka zo da bututun shan ruwa da kwanduna na zinariya, azurfa da lu’ulu’u na Aljanna, sannan suka kawo wa Amina wasu abubuwan sha daga Aljanna, ta sha. Bayan haihuwarsa, an yi masa wanka da ruwan Aljanna, sannan aka shafa masa turaren Firdausi.
Mu’ujizojin haihuwar Annabi
A ranar haihuwar Annabi, duk wani gunki da yake ko’ina a duniya ya fadi da fuskarsa kasa. Guda goma sha hudu daga cikin ginshikan fadar Kisra sun rushe. Tafkin Sawa, wanda ake bautawa, ya bushe ya koma wajen gishiri. A kwarin Sawa, inda shekaru da dama ba a taba ganin ruwa ba, ruwa ya fara gudana. Wutar gidan bautar Farisa wadda ba ta taba mutuwa ba tsawon shekaru dubu, ta mutu a daren haihuwar Annabi. Ilimin bokaye da sihirin masu sihiri sun rushe, kuma rufin Kisra ya tsage gida biyu, wanda har zuwa yau ake iya ganinsa.
A lokacin haihuwarsa, an ji wannan kira daga sama:
«وَجَاءَ الْحَقُّ وَزَهَقَ الْبَاطِلُ ۚ إِنَّ الْبَاطِلَ كَانَ زَهُوقًا...»
(Suratul Isra’i, aya ta 81)
Siffofin Annabi
Kuda bai taba sauka a jikinsa mai daraja ba. Idan idanunsa masu daraja suka yi barci, zuciyarsa tana a farke tana gani da ji. Annabi yana ganin abin da yake bayan sa kamar yadda yake ganin abin da yake gabansa.
Duk dabbar da ya hau ba ta taba tsufa ko ta rame ba. Yana da jaki mai suna Ya’afur. Duk lokacin da ya umurci jakin da ya kawo wani mutum, yana zuwa kofar gidansa, ya buga kansa a kofa, sannan da ishara ya sa a kawo mutumin.
Daga cikin kebantattun abubuwan haihuwar Annabi akwai cewa an haife shi da kaciyarsa, cibiyarsa ta riga ta yanke, kuma yana tsarkakakke daga kazanta ta jini da makamantansu. Haka kuma lokacin haihuwa ya fito da kafafunsa ba da kansa ba. A lokacin haihuwa ya fuskanci Ka’aba ya yi sujjada, sannan bayan ya daga kansa daga sujjadar ya daga hannayensa zuwa sama ya tabbatar da kadaitar Allah da manzancinsa. Daga nan wani haske ya fita daga gare shi wanda ya haskaka gabas da yammacin duniya.
Mu’ujizan Annabi
Annabi yana da mu’ujizai masu yawa, daga cikinsu akwai:
- Karɓuwar addu’arsa wajen tayar da matattu, dawo da ganin makafi da warkar da marasa lafiya.
- Maganarsa da dabbobi.
- Sanin dukkan harsuna da kuma ikon yin magana da dukkaninsu.
- Hatimin annabta yana a bayan sa mai daraja, kuma haskensa ya fi hasken rana ƙarfi.
- Ruwa ya rika gudana daga tsakanin yatsunsa masu daraja har jama’a suka sha suka ƙoshi.
- Tsakuwa tayi tasbihi a hannunsa mai daraja, kuma mutane suna ji.
- Jikinsa mai daraja ba shi da inuwa a hasken rana.
- Duk lokacin da ya zuba yawunsa mai daraja a rijiya, albarka tana bayyana a cikinta kuma ta cika da ruwa. Idan aka shafa yawunsa mai daraja ga mai wata cuta, yana samun waraka.
- Duk abincin da hannunsa mai daraja ya taba yana samun albarka, kuma daga ƙanƙanin abinci yana ciyar da mutane masu yawa.
- Idan yana tafiya a kasa mai laushi, sawun ƙafarsa ba ya fitowa; amma idan yana tafiya a kan dutse mai tauri, alamar sawunsa tana bayyana.

Haihuwar Imam Sadiƙ (amincin Allah ya tabbata a gare shi)
A ranar 17 ga watan Rabi’ul Awwal na shekara ta 83 bayan hijira, an haifi Imam Ja’afar Sadiƙ a Madina mai daraja. Sunansa mai albarka Ja’afar ne, kunyarsa mai girma Abul Abdullah ce, lakabinsa mai haske kuma Sadiƙ ne. Mahaifinsa mai daraja shi ne Imam Muhammad Baqir, mahaifiyarsa mai girma kuma ita ce Ummu Farwa. Imam Sadiƙ ya ce game da ita: “Mahaifiyata tana daga cikin mata masu imani, masu tsoron Allah da masu kyautatawa; kuma Allah yana son masu kyautatawa.”
Imam Sadiƙ yana da ‘ya’ya maza bakwai da mata uku, su ne: Imam Musal Kazim (amincin Allah ya tabbata a gare shi), Isma’il, Abdullah, Muhammad Dibaj, Ishaq, Ali Aridhi, Abbas, Ummu Farwa, Asma’u da Fatima.
A cikin siffofinsa an ambata cewa ya kasance matsakaicin tsawo, fuskarsa mai haske, jikinsa fari, hancinsa mai tsaho, gashinsa baki ne mai murɗewa, kuma akwai wani baƙin tabo a kumatunsa.
Ayyukan ranar albarka ta 17 ga Rabi’ul Awwal
Ranar haihuwar Annabi rana ce mai daraja da albarka wadda tun zamanin da salihai daga zuriyar Muhammad (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa) suka kiyaye girmanta, suka sauke hakkinta, kuma suka yi azumi a cikinta.
Duk wanda ya yi azumin 17 ga Rabi’ul Awwal, Allah Maɗaukaki zai ba shi ladan azumin shekara guda. A wannan rana ana so a yi sadaka, ziyartar wuraren ziyara masu tsarki, yin ayyukan alheri, da faranta ran muminai.