Most searched:

Yaƙin Banu Nadir; wani abin koyi ne na basira da jaruntakar Amirul Mu’uminin (A.S)

A ranar 22 ga watan Rabi'ul Awwal na shekara ta huɗu bayan Hijira, Madina ta shaida kawo ƙarshen fitinar da Banu Nadir suka tayar sakamakon karya alkawarinsu; lamarin da ya ƙare da babbar nasara da korar da ta zama abin darasi, tare da jarumtar Amirul Mu'uminin (Amincin Allah ya tabbata gare shi) a gefen Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa).

Yaƙin Banu Nadir shi ne karo na biyu na soja tsakanin rundunar Musulunci da ɗaya daga cikin ƙabilun Yahudawa da ke zaune a Madina. Ya faru ne bayan karya yarjejeniyar rashin kai hari da kuma shirya makirci ga Cikamakin Annabawa (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa). Wannan lamari, wanda ya kai ga bayar da umarnin korar Yahudawan wannan ƙabila da saukar ayoyin Suratul Hashr, ya nuna rawar gani da muhimmiyar gudummawar Amirul Mu’uminin (Amincin Allah ya tabbata gare shi) wajen samun wannan nasara.

Makircin Yahudawa

Makirci da karya alkawarin Banu Nadir sun zo tare da saukar ayoyin Suratul Hashr da kuma kewaye ƙagaransu. A wannan yaƙi, Amirul Mu’uminin (Amincin Allah ya tabbata gare shi), yana ɗauke da tutar Musulunci, ya kasance a sahun gaba wajen murƙushe masu karya alkawari da tabbatar da nasara.

Allah Madaukakin Sarki yana cewa a aya ta 2 ta Suratul Hashr game da ƙungiyoyi uku na Yahudawan Madina — Banu Qainuqa, Banu Qurayza da Banu Nadir — waɗanda suka yi alkawari da Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa) sannan suka karya shi:

«هُوَ الَّذِی أَخْرَجَ الَّذِینَ کَفَرُوا مِنْ أَهْلِ الْکِتابِ مِنْ دِیارِهِمْ لِأَوَّلِ الْحَشْرِ ما ظَنَنْتُمْ أَنْ یَخْرُجُوا،

“Shi ne Wanda Ya fitar da waɗanda suka kafirta daga Ma’abota Littafi daga gidajensu a farkon fitarwar. Ku muminai ba ku yi zaton za su fita ba.”

A lokacin da alkawari ke tsakanin Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa) da Yahudawan Madina, Manzon Allah ya je wurin mutanen Banu Nadir domin neman taimako wajen biyan diyyar mutane biyu da ɗaya daga cikin Sahabban Cikamakin Annabawa ya kashe bisa kuskure. A can ya gana da Ka’b bin Ashraf, ɗaya daga cikin manya kuma attajiran Yahudawa.

Ka’b ya ce: “Aminci ya tabbata gare ka, Abul Qasim, maraba.” Sannan ya tashi yana nuna kamar zai je ya kawo abinci, alhali a zuciyarsa yana ƙulla shirin kashe Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa) da Sahabbansa ne.

Kafin Ka’b ya aiwatar da makircinsa, mala’ika Jibrilu (Amincin Allah ya tabbata gare shi) ya sauko wurin Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa) ya sanar dashi. Nan take Manzon Allah ya koma Madina, sannan ya tura Muhammad bin Maslama al-Ansari zuwa wurin Banu Nadir domin isar musu da wannan saƙo mai tsauri: “Allah Ya sanar dani makircin da kuka ƙulla; saboda haka ko ku fita daga ƙasarmu, ko kuma ku shelanta layin yaƙi.” Da farko sun amince da barin ƙasar.

Farkon Kewayewa 

A daidai wannan lokaci, Abdullah bin Ubayy, ɗaya daga cikin munafukan Madina kuma abokin haɗin gwiwar Yahudawan Banu Nadir, ya aika musu da saƙo cewa: “Kada ku fita. Ku zauna ku shelanta layin yaƙi da Muhammad. Ni da mutanena da abokan haɗin gwiwarmu zamu taimake ku. Idan kuka fita, zan fita tare da ku; idan kuma kuka yi yaƙi, zan yi yaƙi tare da ku a kansu.”

Banu Nadir suka zauna a cikin ƙagaransu, suka ƙarfafa wuraren tsaronsu kuma suka shirya yaƙi. Sannan suka aika wa Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa) da saƙo cewa: “Ba zamu fita daga nan ba; ka yi duk abin da kake so.”

Da Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa) ya ji wannan saƙo, ya yi kabbara, Sahabbansa ma suka yi kabbara tare dashi.

Sannan Manzon Allah ya ce wa Amirul Mu’uminin (Amincin Allah ya tabbata gare shi): “Ka tafi wajen Banu Nadir.” Amirul Mu’uminin (Amincin Allah ya tabbata gare shi) ya karɓi tutar, ya yi gaba.

Daga nan Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa) ya matsa gaba ya kewaye ƙagararsu. Abdullah bin Ubayy bai cika alkawarinsa ba, ya yaudare su. A ƙarshe, da rundunar Musulunci ta iso, Yahudawan Banu Nadir suka fara ƙoƙarin kiyaye dukiyoyinsu tare da rushe gidajensu domin kada wani abu ya rage wa rundunar Musulunci. [1]

Shelanta Yaƙi

Bayan karya alkawari da makircin Banu Nadir, Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa) ya bayar da umarnin kewaye ƙagaransu. A wannan arangama, Amirul Mu’uminin (Amincin Allah ya tabbata gare shi), yana ɗauke da tutar rundunar Musulunci, ya taka muhimmiyar rawa wajen murƙushe cin amana da fitar da masu karya alkawari daga Madina.

Abdullah bin Ubayy — ɗaya daga cikin munafukan Madina kuma abokin haɗin gwiwar Yahudawan Banu Nadir — ya aika wa Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa) da saƙo cewa: “Ba zamu fita daga gidajenmu da ƙasarmu ba; ka yi duk abin da kake so!”

Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa) ya yi kabbara, Musulmai ma suka ɗaga murya da kabbara tare dashi, sannan ya ce: “Yahudawa sun tashi yaƙi.”

Sannan Manzon Allah ya tafi zuwa wurinsu tare da Sahabbansa, ya yi sallar La’asar a fili a ƙasar Banu Nadir. A wannan tafiya, tutar Musulunci tana hannun Amirul Mu’uminin Imam Ali bin Abi Ɗalib (Amincin Allah ya tabbata gare shi), yayin da Manzon Allah ya bar Ibn Umm Maktum a matsayin wakilinsa a Madina.

Kewayewa da Kora

Ƙare kewayewa Banu Nadir da fitar su daga Madina ya ƙarfafa ikon al’ummar Musulunci tare da kawo ƙarshen karya alkawarin wannan ƙabila. Da wannan lamari, dukiyoyi da kayan aikin da suka bari suka shiga hannun Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa), domin ya sarrafa su da basira wajen tafiyar da al’amuran Musulmai.

Da Yahudawan Banu Nadir suka ga Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa), suka hau saman ƙagaransu suka shirya duwatsu da kibiyoyi. Amma a wannan lokaci Banu Qurayza suka nisanta kansu daga gare su, basu taimaka musu da komai ba. Haka kuma Abdullah bin Ubayy da abokan haɗin gwiwarsu daga ƙabilar Ghatafan suka bar su su kaɗai.

Banu Nadir, bayan sun yanke ƙauna daga samun kowane irin taimako, suka makale a cikin ƙagaransu. Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa) ya kewaye su kuma ya sare itatuwan dabinonsu. Sai suka ce: “Zamu fita daga ƙasarka.”

Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa) ya ce: “A yau ba zan ƙara karɓar wannan tayin ba. Ku fita daga nan. Rayukanku suna cikin aminci, kuma duk abin da raƙumanku zasu iya ɗauka naku ne, ban da makamanku.” Yahudawan suka amince da wannan sharaɗi.

Bayan kwanaki 15 na kewayewa, da hannayensu suka rushe gidajensu. Sannan Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa) ya kore su daga Madina, ya ɗora wa Muhammad bin Maslama alhakin fitar dasu. Suka ɗora matansu da ‘ya’yansu kan raƙuma 600 sannan suka yi ƙaura.

Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa) ya ce: “Matsayin waɗannan a tsakanin mutanensu kamar matsayin Banu Mughira ne a tsakanin Quraysh.” Suka nufi Khaybar, yayin da munafukai suka yi matuƙar baƙin ciki saboda tafiyarsu.

Dukiyoyi da makaman da Banu Nadir suka bari, waɗanda suka haɗa da sulke 50, hulunan ƙarfe 50 da takubba 340, suka shiga hannun Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa).

Waɗannan dukiyoyi sun kasance na musamman ga Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa), kuma an ajiye su domin bukatunsa da abubuwan da zasu taso. Manzon Allah bai ware khumsi daga cikinsu ba, kuma bai sanya wa kowa rabon gama gari ba. Duk da haka, ya baiwa wasu daga cikin Sahabbansa wani ɓangare daga cikinsu, sannan ya yi amfani dasu wajen sauƙaƙa wa mutane al’amuransu. [2]

Jarumtakar Shugaban Masu Taqawa

Makircin dare na kai hari kan alfarmar Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa) a lokacin yaƙin Banu Nadir ya rushe sakamakon martani mai ƙarfi da sauri. Wannan lamari yana ba da labarin jarumtaka da kaifin basirar Amirul Mu’uminin (Amincin Allah ya tabbata gare shi) wajen tsaron martabar Manzanci, inda ya rusa makircin maƙiya tun daga matakan farko.

Lokacin da Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa) ya tafi wajen Banu Nadir — waɗanda wasu Yahudawa ne dake zaune kusa da Madina, kuma lokaci zuwa lokaci sukan cutar da Musulmai idan suka samu dama — da ya isa gindin ƙagaransu da hasumiyoyinsu da ganuwarsu, ya bayar da umarnin a kafa rumfarsa a mafi ƙasƙancin wurin ƙasar, wato “Ƙasar Banu Hadma”.

Da dare ya yi, wani mutum daga Banu Nadir ya harba kibiya zuwa rumfar Manzon Allah, kibiyar kuma ta bugi rumfarsa. Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa) ya bayar da umarnin a mayar da alfarwar zuwa gangaren wani dutse, sannan Muhajirai da Ansar suka kewaye rumfarsa da labule.

Da duhu ya mamaye ko’ina, ba a ga Amirul Mu’uminin (Amincin Allah ya tabbata gare shi) ba. Mutane suka ce: “Ya Manzon Allah, ba ma ganin Imam Ali bin Abi Ɗalib (Amincin Allah ya tabbata gare shi); mun rasa inda yake.”

Manzon Allah ya ce: “Ina tsammanin ya tafi ne domin gyara wani al’amarin da ya shafe ku.”

Ba da daɗewa ba Amirul Mu’uminin (Amincin Allah ya tabbata gare shi) ya dawo ɗauke da kan mutumin Yahudawan nan da ya harba kibiya zuwa rumfar Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa), wanda sunansa Azur, sannan ya ajiye kan a gaban Manzon Allah.

Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa) ya tambaya: “Ya Imam Ali, me ka yi?”

Imam Ali bin Abi Ɗalib (Amincin Allah ya tabbata gare shi) ya ce: “Na ga wannan mugun mutum jarumi ne kuma mara tsoro, sai na yi masa kwanton ɓauna. Na ce a raina: Mene ne ya sa ya zama mara tsoro haka a cikin duhun dare, in ba domin yana son ya kawo mana farmaki da bazata ba? Wannan kuma abu ne mai yiwuwa. Ba zato sai na gan shi yana tahowa da takobi tsirara a hannunsa tare da Yahudawa uku. Na kai masa hari na kashe shi, waɗanda suke tare dashi kuma suka gudu. Har yanzu basu yi nisa ba; ka tura wasu mutane tare dani, ina fatan zamu riske su.”

Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa) ya tura mutane 10 tare dashi, daga cikinsu akwai Abu Dujana da Sahl bin Hunaif. Suka bi su, suka riske su kafin su fake cikin ƙagara, suka kashe su sannan suka kawo kawunansu wurin Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa). Manzon Allah ya bayar da umarnin a jefa kawunan cikin rijiyoyin Banu Hadma.

Cin Ƙagarun Banu Nadir

Cin nasara kan Banu Nadir da gudanar da ganimar farko ya zama farkon wata al’ada mai ɗorewa ta waqafi a Musulunci. Ta hanyar basirar Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa) da kulawar Amirul Mu’uminin (Amincin Allah ya tabbata gare shi), wannan gado mai ɗorewa ya ci gaba da kasancewa a hannun zuriyar Sayyada Fadima (Amincin Allah ya tabbata gare ta) har zuwa yau.

Wannan lamari ne ya kai ga cin ƙagarun Banu Nadir, kuma a wannan daren aka kashe Ka’b bin Ashraf. Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa) ya karɓi dukiyoyinsu; wannan ita ce dukiya ta farko da ta shiga hannunsa, sannan ya raba ta tsakanin Muhajirai na farko. Manzon Allah ya umarci Amirul Mu’uminin (Amincin Allah ya tabbata gare shi) da ya tattara rabon Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa).

An mayar da wannan rabo waqafi, kuma ya kasance a hannun Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa) tsawon rayuwarsa. Bayan rasuwarsa, ya kasance a hannun Amirul Mu’uminin (Amincin Allah ya tabbata gare shi), kuma har zuwa yau yana hannun zuriyar Sayyada Fadima (Amincin Allah ya tabbata gare ta). [3]

Madogara
[1] Bihar al-Anwar, juzu’i na 20, shafi na 168; Tafsir al-Qummi, juzu’i na 2, shafi na 358; Tafsir al-Burhan, juzu’i na 5, shafi na 332
[2] al-Dabaqat al-Kubra, juzu’i na 2, shafi na 57
[3] al-Irshad, juzu’i na 1, shafi na 92

Ƙarin abubuwa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *