Shugaban muminai (A.S) ya yi wasiyya ga ‘ya’yansa, Imam Hassan (A.S) da Imam Husain (A.S) da kuma sauran iyalansa, da su boye kabarinsa bayan shahadarsa; domin ya sani cewa mulki zai fada hannun Umayyawa, kuma su saboda gaba da kiyayya, ba zasu kaurace wa tono kabarinsa ba.
Imam Husain (A.S) ya nakalto:
«An fitar da gawar shugaban muminai (A.S) da daddare daga gida, sun wuce ta gefen masallacin “Ash’ath” sannan aka binne shi a yankin “Ghari” kusa da Najaf. Bisa wasiyya, an boye mazaunin kabarin domin ya kasance a amince daga sharrin Bani Umayya.»
Safwan al-Jammal ya tambayi Imam al-Sadiq (A.S):
«Me ya sa Ahlul Baiti (A.S) ba su bayyana kabarin shugaban muminai (A.S) ba? Imam ya amsa: Saboda tsoron cutarwar Bani Marwan da Khawarij.»
Imam al-Baqir (A.S) ya ruwaito:
«Shugaban muminai (A.S) ya wasiyyar wa Imam Hassan da Imam Husain (A.S) cewa su binne shi da daddare tare da taimakon wasu mutane kalilan, sannan su mayar da wurin kabarin madaidaici (daidai da kasa).»
Imam al-Sadiq (A.S) ya ce:
«Yayin shahadar shugaban muminai (A.S), Imam Hassan da Husain (A.S) tare da wasu mutane biyu daban sun fitar da gawarsa daga Kufa suka nufi makabartu, inda suka binne shi a “Ghari” suka kuma gyara kasar wurin ta zama madaidaiciya.»
Shugaban muminai (A.S) ya umarci dansa Imam Hassan (A.S) da ya haka kaburbura hudu a wurare daban-daban: a cikin masallaci, a cikin Rahbah (filin masallacin Kufa), a Ghari (Najaf ta yanzu), da kuma a gidan Ja’ada bin Hubairah (daya daga cikin sahabban Manzo). Manufar hakan ita ce domin makiyansa kada su samu damar gano takamaiman wurin kabarin na gaskiya.
Sheikh Mufid ya ruwaito:
«Imam Hassan (A.S) da Imam Husain (A.S) sun gudanar da wankan gawa da likafanin mahaifinsu bisa wasiyyar sa, suka tafi da gawarsa zuwa Ghari (Najaf) suka binne shi a can. Sannan suka boye mazaunin kabarin don kada Bani Umayya su samu damar isa gare shi. Kabarin shugaban muminai (A.S) ya kasance a boye har zuwa zamanin Imam al-Sadiq (A.S), inda ya bayyana mazauninsa a lokacin daular Abbasiyawa.»
Ahlul Baiti (A.S) sun kasance masu matukar kiyayewa, inda suke sanar da mazaunin kabarin ga mabiya (Shi’a) na musamman wadanda suke boye sirri kawai. Wani lokaci don kare ran mabiya da na kansu, sukan yi amfani da amsoshi masu sarkakiya; misali, lokacin da Ishaq bin Abdullah (mai ra’ayin Umayyawa) ya tambayi Imam al-Baqir (A.S) inda kabarin yake, sai ya amsa da cewa: «An binne shi da daddare a Kufa, kuma takamaiman wurin ban sani ba.»
“Ibn Dawus” yayin bayyana daya daga cikin ruwayoyin ya ce:
«Idan mai ruwaya ba amintacce ba ne, yana iya yiwuwa maganarsa kuskure ce ko kuma ya fada ta ne a boye da gangan, domin kuwa kabarin shugaban muminai (A.S) an boye shi ne da gangan kuma babu wanda aka sanar da shi a bayyane.»
“Ibn Abi al-Dunya”, masanin hadisi da tarihin Bagadaza, ya nakalto:
Lokacin da aka tambayi wasu manyan mutane: Shin wani ya yi sallah a kan gawar Amirul Muminina Ali (A.S) ko ya shaidi binne shi? Suka ce: A’a. Amma Muhammad bin Sa’ib ya ce: «Imam Hassan, Husain, Muhammad bin Hanafiyyah da Abdullah bin Ja’afar tare da wasu gungun danginsu ne suka fitar da gawar shugaban muminai (A.S) da daddare suka binne shi a bayan Kufa. Dalilin wannan aikin shi ne tsoron tono kabarin da Khawarij ko makiya zasu iya yi.»
“Ibn Abi al-Hadid” shi ma ya nakalto:
«Abul Qasim al-Balkhi ya ce Bani Umayya suna son cutar da kabarin Imam. Saboda haka ‘ya’yansa suka boye mazaunin binne shi kuma suka rudar da mutane ta hanyoyi daban-daban. Misali, sun dora wani akwati a kan rakumi don nuna kamar zuwa Madina zasu kai shi. Ko kuma suka yi gawar jabu suka dora a kan kaya don a ce a “Hirah” aka binne shi, ko kuma suka haka kaburburan alama a wurare daban-daban kamar masallacin Kufa, fadar gwamnati, gidaje har ma da daji.
Ta wannan hanyar, babu wanda ya san mazaunin asali na kabarin sai ‘ya’yansa da wasu sahabbansa na kusa sosai. Su ne suka binne shi a asubar daren ashirin da daya ga watan Ramadana a yankin Ghari (Najaf), bisa wasiyyar Imam din kansa. Daga washegari, jita-jita masu yawa suka bazu game da mazaunin kabarin, inda kowane rukuni yake fadin abin da ya ga dama. Har ma wasu sun yada jita-jitar cewa wata kabila daga “Tayyi” sun hadu da rakumin da yake dauke da akwatin, suka zata akwatin dukiya ne, lokacin da suka fahimci gaskiya, sai suka binne shi, suka yanka rakumin suka cinye! Wannan jita-jitar ta shahara tsakanin Bani Umayya da mabiyansu kuma wasu sun yarda da ita.»
“Ibn Hajar al-Asqalani” ya ce:
«An boye kabarin shugaban muminai (A.S) ne don kada Khawarij su tono shi.»
Ibn Dawus ya yi kararin bayani:
«Shugaban muminai (A.S) ya yi wasiyyar boye kabarinsa ne saboda tsoron gaba ta Bani Umayya, Khawarij da sauran makiya. Idan har kabarinsa ya fito fili makiyansa suka tona shi, to wannan zai iya haddasa yaki da rigima tsakanin Bani Hashim da makiyansu, al’amarin da Imam ya kasance yana guje masa tun lokacin rayuwarsa. Boye kabarin yana da fa’idodi wadanda dalla-dallansu ba su kai gare mu ba.»
“Hassan bin Muhammad al-Dailami” shi ma ya rubuta:
«Kiyayya ga shugaban muminai (A.S) ta fara ne tun lokacin Manzo (S.A.W) har bayan shahadarsa. Hatta Ibn Muljam (makashin Imam) lokacin da aka kama shi ya ce: “Da zan iya, da na yanke kunnen Hassan bin Ali!” Tun da irin wannan kiyayya ta fito daga mutum guda, to halin Mu’awiya da Bani Umayya da mabiyansu wadanda mulki yake hannunsu ya fito fili. Sun yi kokari sosai wajen kashe hasken Ahlul Baiti. Saboda wannan dalilin, shugaban muminai (A.S) ya yi wasiyyar binne shi a asirce don kada a keta alfarmar kabarinsa.»
“Ala’uddin Ali Dade” ya ce:
«Imam na farko da aka boye kabarinsa shi ne Ali bin Abi Talib (A.S), domin ya sani cewa mulki zai koma hannun Bani Umayya kuma suna iya yin abubuwa marasa kyau ga kabarinsa. A zamanin Bani Umayya, Hajjaj bin Yusuf ya yi kokarin gano inda kabarin shugaban muminai (A.S) yake, inda ya ba da umarnin tono kaburbura kusan dubu uku a Najaf al-Ashraf, amma ba su samu nasara ba.»
Muhammad Baqir al-Khansari shi ma ya yi ishara da wannan lamarin. Ya ce: «Godiya ta tabbata ga Allah da ya sanya Hajjaj bai samu nasara ba duk da dukkan kokarinsa.»
Madogara:
An ciro daga littafin «Tarihin Haikali Mai Alfarma na Alawi» (Tarikh al-Marqad al-Alawi al-Mutahhar).