Abubuwan da ke tafe a kasa, takaitaccen bayani ne kan sirri da rayuwar Amirul Muminina (A.S).
“Idan zuciya tana son sanin Allah, to ta kalli fuskar Ali duka; Na san Ubangiji ne ta hanyar Ali, na rantse da Allah.”
Suna: Ali bin Abi Ɗalib (A.S)
Sunan Uba: Abu Dalib, Abdul Manaf dan Imran
Sunan Uwa: Faɗima bint Asad bin Hashim
Sunan Kaka: Abdul Muɗallib bin Hashim
Sunan ‘Yan’uwa Maza: Ɗalib, Aqil, Ja’afar
Sunan ‘Yan’uwa Mata: Ummu Hani, Jumana
Rana da Wurin Haihuwa: An haifi Amirul Muminina (A.S) a ranar Jumma’a, sha uku ga watan Rajab a cikin dakin Ka’aba mai alfarma, shekaru talatin bayan haihuwar Annabi Mai Tsira da Aminci (S.A.W.A).
Karbar Musulunci: Shi ne mutum na farko da ya karbi Musulunci.
Shahararrun Mata: Faɗima Al-Zahra (A.S), Ummul Banin bint Hizam bin Khalid bin Darim Al-Kilabiyya, Layla bint Mas’ud Al-Darimiyya, Asma bint Umais Al-Khath’amiyya, Khawlah bint Ja’afar bin Qais Al-Khath’amiyya, Ummu Habib bint Rabi’ah, Ummu Sa’id bint Urwah bin Mas’ud Al-Thaqafi.
‘Yayye Maza: Hassan (A.S), Hussein (A.S), Muhsin, Muhammad (wanda ake yi wa lakabi da Abu Qasim kuma aka sani da Ibn Hanafiyya), Abbas (Abul Fadl), Amru, Ja’afar, Usman, Abdullah, Muhammad Al-Asghar (wanda ake yi wa lakabi da Abu Bakr), Ubaidullah, Auna da Yahya.
‘Yayye Mata: Zainab Al-Kubra (A.S), Zainab Al-Sughra (wacce ake yi wa lakabi da Ummu Kulsum), Ruqayya, Ummu Hassan, Ramlah, Nafisa, Ruqayya Al-Sughra, Ummu Hani, Ummu Kiram Jumana (wacce ake yi wa lakabi da Ummu Ja’afar), Umamah, Ummu Salama, Maimuna, Khadija da Faɗima.
Kunayoyin Amirul Mu’uminina (A.S): Abu Hassan, Abu Hussein, Abu Sabtain, Abu Raihanatain, Abu Turab; wannan kunyoyi ce da Manzon Allah (S.A.W.A) ya ba wa Amirul Mu’uminina (A.S).
lakabobin Amirul Mu’uminina (A.S): Amirul Mu’uminina, Murtadha, Wasiyyi, Haidar, Ya’asubul Mu’uminina, Ya’asubuddin.
Siffofin Amirul Mu’uminina (A.S)
1- An haifi Amirul Mu’uminina (A.S) a cikin dakin Ka’aba mai alfarma, inda babu wanda aka taba haifa a wannan wuri mai albarka kafin shi.
2- A lokacin da Annabi (S.A.W.A) ya kulla sabbin ‘yan’uwantaka tsakanin Musulmi, shi da kansa ya kulla alkawarin ‘yan’uwantaka da Amirul Mu’uminina (A.S).
3- Shi ne mai rike da tutar Annabi Mai Tsira da Aminci (S.A.W.A).
4- Annabi Mai Tsira da Aminci (S.A.W.A) ya kasance yana mika wa Amirul Mu’uminina (A.S) jagorancin yake-yake.
5- Amirul Mu’uminina (A.S) ne ya isar da ayoyi da ma’anonin Suratul Taubah ga mutane a madadin Annabi (S.A.W.A).
Ba’adin Amirul Mu’uminina (A.S): A ranar takwas ga watan zhul-Hijjah shekara ta goma bayan hijira, a rumbun ruwa na Ghadir Khum bisa umarnin Manzon Allah (S.A.W.A), mutane suka yi mubaya’a ga Amirul Mu’uminina (A.S) domin ya gaje shi, amma ya kai ga karbar mulki na zahiri a watan zhul-Hijjah shekara ta 35 bayan hijira.
Wurin Mulki na Zahiri: Kufa.
Mawaƙan Amirul Mu’uminina (A.S): Najashi, Al-A’awar Al-Shani.
Rubutun Jikin Zobe: Allahu Al-Malik wa Aliyyun Abduhu.
Yake-yake: Jamal, Siffin, Nahrawan.
Tuta: Tutar Manzon Allah (S.A.W.A).
Ayyuka: Nahjul Balagha.
Marubuci: Abdullah bin Abi Rafi.
Shahada: Amirul Mu’uminina (A.S) ya fadi a kan shimfida sakamakon saran da “Abdurrahman bin Muljam Al-Muradi Al-Khariji” ya yi masa a daren sha tara ga watan Ramadan mai alfarma na shekara ta arba’in bayan hijira, alhali yana tsaye yana sallar asuba a masallacin Kufa, kuma ya yi shahada a daren ashirin da daya ga wannan wata.
Kabari Mai Tsarki: Imam Hassan (A.S) ya binne gawar imam mai tsarki a yankin “Al-Ghari” wato Najaf Al-Ashraf, kuma ya boye wannan kabari domin takiyya saboda Khawarij da Mu’awiya, har ya zuwa yau inda kabarin imam mai tsarki yake takama da koli da daukaka tare da samaniya.