Sashen Harkokin Mata na Atabutul Alawiyya, a cikin shirye-shiryen karo na biyar na Makon Sadiqai na Ƙasa da Ƙasa, ya gudanar da taron tattaunawa mai taken «Mace a cikin Koyarwar Imam Sadiq (amincin Allah ya tabbata a gare shi): Wayewa, Saƙo da Gina Mutum.»
An gudanar da taron ne tare da halartar wasu malaman jami’a, masu bincike da mata masu fafutuka a fannonin tunani da tarbiyya. A yayin taron, an tattauna tushen tarbiyya da ɗaukakar mace a cikin koyarwar Imam Sadiq (amincin Allah ya tabbata a gare shi), da kuma rawar da take takawa wajen tarbiyya da gina mutane al’ummomi masu zuwa.
Batutuwa na Tunani da Tarbiyya
A tarurrukan ranar farko, an tattauna batutuwa da suka haɗa da tsarin ruhaniya da ɗabi’ar mace a cikin koyarwar Imam Sadiq (amincin Allah ya tabbata a gare shi), tushen tarbiyya wayayya a cikin mahangar sa, da kuma rawar da take takawa wajen cikin wayewar tunani wajen fuskantar ƙalubale da karkacewar tunani da al’adu.
Haka kuma, an tattauna hanyoyin ƙarfafa kasancewar mata da rawar da suke takawa a fannoni daban-daban na rayuwa, bisa tsarin tarbiyya da ilimi na koyarwar Imam Sadiq (amincin Allah ya tabbata a gare shi).
Daga Ilimi zuwa Gina Mutum
A tarurrukan rana ta biyu, an binciki hanyoyin amfani da koyarwar Imam Sadiq (amincin Allah ya tabbata a gare shi) a cibiyoyin zamani da suka shafi harkokin mata. Haka kuma an mai da hankali kan rawar mace wajen wucewa daga matakin samun ilimi zuwa amfani da shi wajen tarbiyya da renon Tsararrki masu zuwa.
Daga cikin sauran batutuwan da aka tattauna akwai tushen gina halayen mata masu iya ganewa,wajen yin zaɓi cikin wayewa da kuma tunkarar sauye-sauyen tunani da al’adu cikin ɗaukar alhaki.
Kallo na Zamani ga Koyarwar Imam Sadiq (amincin Allah ya tabbata a gare shi)
Ramla Khuzai, mai kula da Sashen Harkokin Mata, ta bayyana cewa: «Girmama tunawa da sunan Imam Sadiq (amincin Allah ya tabbata a gare shi) wata dama ce ta sake duba gadonsa na ilimi da tarbiyya da kuma amfani da tushensa wajen ƙara wayewa da ƙarfafa rawar da mata ke takawa.»
Ta ƙara da cewa: «An gudanar da wannan taro ne domin sake duba waɗannan tushe da haɗa su da hakikanin rayuwar mata a wannan zamani, domin taimakawa wajen ƙarfafa kasancewarsu a cikin al’umma da ƙara musu ƙwarewar fuskantar ƙalubalen tunani da al’adu bisa ƙa’idojin Musulunci.»
Shirye-shiryen Makon Sadiqai
An gudanar da wannan taro ne a cikin shirye-shiryen tunani da al’adu na Sashen Harkokin Mata a Makon Sadiqai. Waɗannan shirye-shirye suna da nufin ƙarfafa ilimi da sani da aka samo daga gadon Ahlul Baiti (amincin Allah ya tabbata a gare su), da kuma gabatar da batutuwan da suka shafi mace, tarbiyya da gado. Haka kuma suna neman taimakawa wajen gina mutum da al’umma bisa tushen ilimi da ƙa’idojin ɗabi’a.








