Most searched:

Atabutul Alawiyya ta Karrama Masu Hidima 1,000

Atabutul Alawiyya ta karrama masu hidima 1,000 daga ƙungiyoyi da cibiyoyin hidima 40 daga jihohi daban-daban na Iraki.

Cibiyar “Qanbar” ta musamman ga masu hidimar Atabutul Alawiyya, a cikin shirye-shiryen taro karo na biyar na Makon Sadiqain na Ƙasa da Ƙasa, ta gudanar da bikin karrama masu hidima 1,000 daga fiye da ƙungiyoyi da cibiyoyin hidima 40 daga jihohi daban-daban na Iraki.

An gudanar da bikin ne domin nuna godiya ga ƙoƙarinsu wajen ba da hidima ga maziyarta a duk tsawon shekara, musamman a lokutan ziyara da miliyoyin maziyarta ke halarta. Ihsan al-Da’i, Mataimakin sakataren Atabutul Alawiyya, mambobin Majalisar Gudanarwa da wasu shugabannin sassa daban-daban na Atabutul Alawiyya sun halarci bikin.

An fara bikin da karatun wasu ayoyi daga Alƙur’ani mai girma, sannan Haidar al-Isawi, mamba a Majalisar Gudanarwar Atabutul Alawiyya, ya karanta jawabin sakataren Atabutul Alawiyya.

A cikin jawabin ya jaddada cewa: “Hidima a Atabar Amirul Mu’uminin (Amincin Allah ya tabbata gare shi) ba aiki ne kawai da muke yi ba; abin alfahari ne, alhaki ne, amana ce kuma nauyin da Allah Ya keɓe mana, Ya kuma ba mu darajar gudanar dashi.”

Al-Isawi ya ƙara da cewa: “Mai hidima na gaskiya shi ne wanda ya ɗauki aikinsa a matsayin ibada, mu’amalarsa da maziyarci a matsayin saƙon hidima, sannan ya ɗauki ikhlasinsa a matsayin tafarki zuwa ga yardar Allah.”

Ya kuma jaddada muhimmancin gudanar da ayyuka cikin tsantseni da ƙwarewa, tare da mu’amala da maziyarta cikin haƙuri, rahama da kyawawan ɗabi’u.

Ahmad al-Zurqani, Shugaban Cibiyar “Qanbar” ta musamman ga masu hidima, ya bayyana wa cibiyar labarai ta Atabutul Alawiyya cewa: “An karrama masu hidima 1,000 ne bisa umarnin sakataren Atabutul Alawiyya, domin nuna godiya ga rawar ƙungiyoyi da cibiyoyin da ke shiga lokutan ziyara, musamman ziyara da miliyoyin maziyarta ke halarta. Irin waɗannan ziyara suna buƙatar gagarumin ƙoƙari da babban matakin daidaitawa tsakanin cibiyoyin hidima daban-daban domin samar da mafi kyawun hidima ga maziyarta.”

Wissam Iskandar, Shugaban Cibiyar “Nazm” ta Rukunin Tsare-tsare da Bunƙasa, ya ce: “An gudanar da wannan biki ne ta haɗin gwiwar Cibiyoyin Qanbar da Nazm. Mun yi ƙoƙarin amfani da damar halartar shugabanni da wakilan ƙungiyoyi domin gudanar da cikakken shirin horaswa a fannoni biyu, na al’adu da na gudanarwa. Haka kuma, an tattauna hanyoyin aiki, daidaitawa ta haɗin gwiwa da shirye-shiryen hidima dake tafe.”

Ayyukan karo na biyar na Makon Sadiqain na Ƙasa da Ƙasa suna gudana ne cikin haɗin gwiwar sassa da rukunoni masu alaƙa a Atabutul Alawiyya. Waɗannan sassa sun yi ƙoƙari wajen kammala ɓangarorin tsari, gine-gine, yaɗa labarai da hidima na shirye-shiryen, gwargwadon matsayi da tsarkin wannan munasaba.

Ƙarin abubuwa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *